Za ku ce kuna da dangantaka ta musamman da Allah? Kamar kowace dangantaka, alaƙar tana ƙarfafuwa idan akwai kyakkyawar sadarwa. Kuna ɗaukar lokaci sosai kuna magana da Allah kamar yadda kuke yi da iyali ko abokai ta saƙonni?
Lokacin da Yesu ya ciyar da mutane 5000 da mu’ujiza wata rana, bai ce wa almajiransa su gama rarraba abinci ga layi na farko sannan su dawo su sake ciyar da wannan layin da suka ciyar ba. Da ya yi haka, mutanen da suke baya a taron da sun zauna da yunwa, suna jin haushi saboda babu abin da aka ba su, alhali wasu sun samu karo na biyu. Amma me yasa haka yake, sai mu tambayi kanmu, cewa miliyoyin mutane sun ji bishara sau da dama kafin wasu su ji ta sau ɗaya?
Girmar da yara cike yake da ƙalubale. Ba wai kawai yana buƙatar ƙarfi da tsara lokaci ba, amma kuma muna buƙatar mu jagoranci ci gaban halayyar ‘ya’yanmu cikin hikima da kulawa.
Me ya sa wasu mutane suke da tausayi da kulawa ga wasu, amma wasu kuwa kullum suna cike da son kai? Shin ma zai yiwu mutum mai son kai ya zama mai tausayi?
To, tambayar ita ce: Me za ku yi idan kuna cikin matsala kuma ba ku san abin da za ku yi ba? Shin kun taɓa shiga hari daga wani da ku kadai ba za ku iya kare kanku daga gare shi ba? Halin ɗabi’a tamu shi ne firgita!